This blog was created by Comrade Jibril Almustapha Gusau. The blog will provide you with sound, authentic and genuine news across the world
Thursday, 22 June 2017
KUNGIYAR MURYAR TALAKA TA KAI TALLAFI A MASALLATAI
Daga: Comrade-Jibreel Almustapha Gusau
A cigaba da ayyukan taimakon al'ummah a cikin wannan wata mai alfarma na Ramadan. Kungiyar Muryar Talaka ta kasa reshen Jihar Zamfara ta bayar da tallafin butocin Alwala kimanin guda Dari da Hamsin (150) ga masallatan dake garin Gusau babban birnin jihar Zamfara.
Da yake jawabin yayi gabatar da tallafin, Shugaban Kungiyar Comrade Hafizu Balarabe Gusau ya bayyana cewa: "Kungiyar Muryar talaka ta bayar da waddannan kaya ne domin bayar da gudunmawarta ga addinin musulunci a cikin wannan wata na Ramadan."
Masallatan da suka amfana da wadannan butoci sun hada, Babban masallacin juma'ah na Tudun Wada, Masallacin Malam Mustapha Ibrahim Sahihi, Masallacin Unguwar Abarma da kuma Babbar Zawuyyar Shehu Balarabe duk a cikin garin Gusau.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment